Hukumar ‘yan sanda ta kasa ta tabbatar da Olatunji Disu a matsayin babban Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), wanda ya tabbatar da nadinsa a matsayin shugaban ‘yan sanda na 23 na kasa.
Majalisar wadda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta tare da halartar gwamnonin jihohi, ta amince da nadin Disu a taronta da ta gudanar a ranar Litinin din da ta seegabata a fadar gwamnati da ke Abuja.
Tun da farko dai, a ranar 24 ga watan Fabrairu ne shugaba Tinubu ya nada Disu a matsayin mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan sanda bayan murabus din Kayode Egbetokun.
KU KARANTA KUMA: Shugaba Tinubu ya nada Tunji Disu a matsayin mukaddashin IGP
Dangane da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulki na 1999 da Dokar ‘Yan Sanda, nadin na bukatar tabbatar da majalisar ‘yan sanda ta kasa kafin karbar mukami bisa ga kwakkwaran dalili.
Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Litinin bayan kammala taron majalisar, kakakin shugaban kasar, Mista Bayo Onanuga, ya ce a yanzu za a rantsar da Disu a matsayin Sufeto-Janar na ‘yan sanda na 23 a ranar Laraba yayin taron majalisar zartarwa ta tarayya.
Shima da yake magana da manema labarai bayan taron, shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce majalisar ta yi nazari sosai kan bayanan Disu kuma ta gamsu da kwazonsa da ayyukansa.
“A tattaunawar da muka yi, mun bi diddigin bayanansa, ayyukansa a ofis da kuma shawarwarin da ya bayar, kuma majalisar ta yi farin cikin amincewa da shawarwarin da aka ba shi na a nada shi babban sufeton ‘yan sanda,” in ji shi.
Dangane da fatawar Majalisar, AbdulRazaq ya lura cewa sabon shugaban ‘yan sandan yana fuskantar manyan ayyuka, musamman a yayin da ake ci gaba da tattaunawa a kasa game da aikin ‘yan sanda.
“Ya rage masa ayyukansa, musamman a wannan zamani da ake magana a kan ‘yan sandan jihar a yanzu, kalubalen suna nan; ya sha fama da shi, ya yi babban aiki da Rapid Response a jihar Legas da kuma babban birnin tarayya Abuja, don haka yana da tarihin da ya nuna zai iya yin aiki.
Shugaban na NGF ya kara da cewa “Akwai babban fata daga jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja, wanda ya kamata ya tsara. Muna yi masa fatan alheri kuma muna fatan yin aiki tare da shi.”
Taron na ranar Litinin din nan da ta gabata ya biyo bayan murabus din tsohon IGP, Kayode Egbetokun a makon jiya.
KU KARANTA KUMA: IGP Kayode Egbetokun yayi murabus
Disu, gogaggen dan sanda ne, wanda ya shafe shekaru da dama yana gogewa a aiki da gudanarwa, a baya ya taba rike mukamin Kwamishinan ‘yan sanda a Jihar Ribas da Babban Birnin Tarayya, da kuma Mataimakin Sufeto-Janar mai kula da Sashen Kariya na Musamman (SPU).
Tabbatar da nasa na nuni da cewa an samu sauyi a tsarin shugabancin rundunar ‘yan sandan Najeriya a daidai lokacin da ake fuskantar kalubalen tsaro a fadin kasar.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya hada da shugaban kasa a taron; Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume; Mai baiwa kasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu; Ministan harkokin ‘yan sanda, Ibrahim Geidam; da shugaban hukumar ‘yan sanda, Hashimu Argung.
Wadanda suka halarci taron sun hada da shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman, gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Ogun, Dapo Abiodun, gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, mataimakan gwamnonin Kogi da Delta.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Ojo da wasu daga cikin ministocin sun halarci taron.
A’isha. Yahaya, Lagos