Take a fresh look at your lifestyle.

SHUGABAN NAJERIYA YA JAJANTAWA WADANDA BALA’IN RUWA YA YI A PAKISTAN

0 295

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajanta wa ambaliyar ruwa irin ta Pakistan, bala’i mafi muni a tarihin kasar. Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje rabin miliyan, wanda ya shafi kusan mutane miliyan 30 tare da kashe sama da 1,000.

Ambaliyar ta yi awon gaba da daruruwan tituna, gadoji da sauran ababen more rayuwa. Shugaba Buhari ya ce Pakistan da al’ummarta na cikin tunani da addu’o’in ‘yan Najeriya yayin da suke fuskantar wannan bala’i na jin kai. Ya kuma yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da sauran Hukumomin Agaji da su dauki matakan gaggawa don taimakawa mutanen da ba su da matsuguni da abinci da kuma miliyoyin da ke bukatar agajin gaggawa.

Aliyu Bello

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *