Take a fresh look at your lifestyle.

Jam’iyyar APC Ta Kara Karfafa Tattalin Arziki Kafin Zaben 2027

27

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ta umurci ko’odinetocinta na jahohi da na shiyya-shiyya da su kara zage damtse wajen fafutukar ganin an gudanar da zaben 2027.

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma ne ya bayar da wannan umarni a yayin taron dabaru na hudu na Renewed Hope Ambassadors Network da aka gudanar a Abuja.

Taron ya biyo bayan zaman farko da kungiyar gwamnonin ci gaba ta shirya a watan Fabrairu a fadar shugaban kasa, wanda ya samu halartar shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.

Gwamna Uzodimma ya ce, an kafa wannan cibiyar sadarwa ne domin inganta ajandar sabunta begen shugaban kasa Bola Tinubu ta hanyar karfafa cudanya a matakin kasa da inganta sadarwa tsakanin gwamnati da ‘yan kasa, musamman a yankunan karkara.

Ya kuma jaddada bukatar masu gudanarwa su rika sadar da manufofin gwamnati da gyare-gyare yadda ya kamata domin kaucewa munanan bayanai da kuma karfafa amincewar jama’a.

“Idan ba mu sanar da mutane yadda ya kamata ba, za a yi wa wannan gwamnati mummunar fahimta,” in ji shi.

Karanta Hakanan: Kungiyar Tallafawa APC Ta Tattauna Al’ummar Kasa Gabanin Zaben 2027

Jigon APC Ya Yabawa Jagorancin Shugaban Kasa Tinubu

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin ta gudanar da gyare-gyare masu tsauri da nufin daidaita tattalin arziki da kuma tabbatar da ci gaban kasa na dogon lokaci, duk da kalubalen da ake fuskanta.

Ya kuma bayyana ci gaban da aka samu a gwamnatin mai ci, ciki har da shirin asusun bayar da lamuni na ilimi na kasa, wanda ya ce sama da dalibai miliyan daya suka amfana.

Gwamna Uzodimma, ya yi gargadin cewa rashin fahimtar da ‘yan adawa ke yi zai iya gurgunta kwarin gwiwar jama’a idan ba a yi maganinsu yadda ya kamata ba.

Shima da yake nasa jawabin, gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi kira da a kara karfafa nasarorin da gwamnati ta samu a matakin jiha, inda ya bukaci da aka tsara dabarun sadarwa domin kaiwa ga al’ummomin kananan hukumomi yadda ya kamata.

Hakazalika, gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya jaddada mahimmancin hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar domin tabbatar da daidaiton sakonni da kuma isar da sako mai inganci a fadin kasa baki daya.

Gwamnonin sun bayyana kwarin guiwar cewa ci gaba da gangamin jama’a zai kara wa jam’iyyar APC goyon bayan jama’a tare da karfafa damarta a zaben 2027.

 

 

A’isha. Yahaya, Lagos

 

Comments are closed.