Asusun bada lamuni na ilimi na Najeriya (NELFUND) ta karyata rahotannin karin alawus-alawus na kula da dalibai a duk wata zuwa ₦25,000 daga ₦20,000.
Daraktan Sadarwa na Dabarun Oseyemi Oluwatuyi a cikin wata sanarwa ya ce asusun ya lura da bayanan karya da ke yawo game da alawus na wata-wata ga daliban da suka ci gajiyar tallafin.
“Domin a fayyace alawus din da aka amince da shi ya kasance ₦20,000 ba ₦25,000 ba kamar yadda aka ruwaito.
“An shawarci ɗalibai da su yi watsi da duk wani bayani da ya saba wa juna kuma su dogara kawai ga tashoshin sadarwa na NELFUND don samun ingantaccen sabuntawa,” in ji Oluwatuyi.
Ta ce “Asusun ya yaba da ci gaba da hadin gwiwar dalibai kuma ya ci gaba da jajircewa wajen samar da gaskiya da inganci da tallafin da ya mayar da hankali kan dalibai a fadin kasar.”
Ta kara da cewa don ƙarin bincike ko taimako, ana iya samun Asusun ta imel a info@nelf.gov.ng ko ta hanyar dandalin sada zumunta na hukuma: X (tsohon Twitter): @nelfun, Instagram: @nelfund, Facebook da LinkedIn: Asusun Lamuni na Ilimi na Najeriya – NELFUND