Take a fresh look at your lifestyle.

Indonesiya: Mutane 3 Ne Suka Mutu, 28 Suka Jikkata A Wani Hatsarin Jirgin Kasa

83

Akalla mutane uku ne suka mutu yayin da 28 suka jikkata bayan da wasu jiragen kasa guda biyu suka yi karo da juna a lardin Java ta Yamma a kasar Indonesiya, kamar yadda hukumomi suka bayyana.

 

Ma’aikatan agajin gaggawa na aiki a ranar Juma’a don kubutar da akalla wasu mutane biyu da har yanzu ke makale a cikin baraguzan motocin da ke cikin layin dogo.

 

Hatsarin ya faru ne lokacin da wani jirgin kasa mai nisa daga birnin na biyu mafi girma a kasar, wato Surabaya, ya yi karo da wani jirgin kasa da ke kusa da Bandung, babban birnin lardin, in ji Adita Irawati, kakakin ma’aikatar sufuri.

 

Hotunan bidiyo daga masu watsa shirye-shirye na gida MetroTV da Kompas TV sun nuna yadda ake taimakon fasinjoji daga cikin motocin , wasu daga cikin su sun tashi daga kan layin dogo gaba daya bayan hadarin da karfe 6:03 na safe agogon kasar.

 

Masu aikin ceto na tantance yadda za a kubutar da mutanen biyu da aka gano a tsakanin motocin, ko da yake ba a san ko suna raye ba.

 

Mutane ukun da suka mutu ma’aikatan jirgin kasa ne direban da mataimakinsa a cikin jirgin kasa da kuma ma’aikaci a cikin jirgin kasa – in ji Ibrahim Tompo, kakakin ‘yan sandan yankin yammacin Java.

 

Fasinjoji 478 ne ke cikin jirgin a lokacin da hadarin ya afku.

 

Kawo yanzu dai ba a bayyana musabbabin hatsarin ba, amma kamfanin jiragen kasa na PT KAI da gwamnatin lardin sun ce za su gudanar da bincike tare da jami’an tsaron sufuri.

 

 

 

ALJAZEERA/Ladan Nasidi.

Comments are closed.