Take a fresh look at your lifestyle.

VP Shettima Ya Ziyarci Maiduguri Domin Hutun Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

295

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya isa birnin Maiduguri na jihar Borno a wata ziyara.

 

Mataimakin shugaban kasar yana jihar shi ne domin hutun Kirsimeti da sabuwar shekara.

Ya sauka a filin jirgin saman Muhammad Buhari da misalin karfe 15:16 agogon GMT.

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Zulum da wasu mambobin majalisar zartarwa ta jihar Borno sun tarbi mataimakin shugaban kasar.

 

Karanta kuma: Kirsimeti: Shugaba Tinubu ya taya Kiristoci murna

Yayin da yake jihar, ana sa ran zai gana da abokan shi na siyasa da dangin shi.

 

Ladan Nasidi.

Comments are closed.