Wata kotu a Kenya ta yanke wa wata jami’ar diflomasiyyar kasar Venezuela hukunci kan kisan da aka yi wa mukaddashin jakadan kasar daga yankin Latin Amurka shekaru 10 da suka gabata a gidanta da ke Nairobi babban birnin kasar.
Rahoton ya ce an samu Dwight Sagaray, wanda shi ne sakatare na farko na ofishin jakadancin Venezuela da laifin kashe Olga Fonseca a ranar 27 ga Yuli, 2012.
An kuma yanke wa wasu ‘yan kasar Kenya uku da aka gurfanar tare da Mista Sagaray da laifi.
An yi wa jami’in diflomasiyyar shari’ar kisan gilla ne bayan da Venezuela ta yi masa kariyar diflomasiyya.
An kashe Ms. Fonseca kasa da makonni biyu bayan ta fara sabon aikinta a Nairobi a ranar 15 ga Yuli, 2012.
Ba a dai san dalilin kisan ba, amma jami’an Kenya sun ce a lokacin wasu ma’aikatan gidan ba su ji dadi ba bayan sallamar da Misis Fonseca ta yi musu
Leave a Reply