Shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa ya kafa dokar ta baci a kasa sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya haifar da ambaliyar ruwa da yayi sanadiyar mutuwar mutane 443 a yankin Durban .
“Majalisar zartaswar tayi taron gaggawa tare da kafa dokar ta baci,” shugaban kasar yace wannan lamari “asarar rayukan jama’ a akayi”.
“Yau kasar mu na cikin zaman makoki,” Mr Ramaphosa, ya ziyaraci yankin a ranar Laraba.
Tuni aka tura dakaru dubu 10,000 zuwa yankin da bala’ in ya faru domin taimakawa wadanda abun ya shafa a yankin KwaZulu-Natal (KZN) inda aka samu asarar rayuka mafi muni.
Kamar yadda masu harsashen yanayi suka fada ,cewa ba za’ a sake samun ambaliyar ruwa ba a cikin kwanaki masu zuwa..
LADAN NASIDI
Leave a Reply