An zabi Kwamred Hussaini Hamisu Yanduna a matsayin sabon shugaban Kungiyar kwadago ta kasa(NLC) reshen jihar Katsina a karo na biyu
An gudanar da zaben ne lokacin babban taron kungiyar wanda ya gudana a dakin taro na sakatariyar jihar dake birnin Katsina
Kwamred Hamisu Yanduna ya samu nasarar komawa kujerar sa ba tare da hamayya ba bayan da dukkanin wakillan kungiyar a wajen taron suka amince ya kasance a matsayin sabon shugaban kungiyar reshen jihar Katsina a karo na biyu
Sauran wadanda aka zaba a matsayin shugabannin kungiyar sun hada da Bishir Amadu a matsayin mataimakin shugaba na daya(I) da Nasiru Wada a matsayin mataimakin shugaba na biyu(II)
Yayin da aka zabi Haruna Mamman a matsayin Ma’ajin kungiyar sai Zailani Isyaku Kofar Bai da Kabir Gambo a matsayin mai binciken kudi na daya(I) da na biyu
Sauran wadanda aka zaban sune A’isha Haruna da Hadiza Mamman Danmusa a matsayin Ex-officio ta daya(I) da ta biyu (II)
A jawabinsa jim kadan bayan jagorantar gudanar da zaben wakilin uwar kungiyar na kasa kwamred Aliyu Ado Minjibir wanda kuma shine mataimakin shugaban kungiyar(NLC) na kasa ya bayyana zaben a matsayin Sahihi kuma amintacce, yana mai kira ga zababbun shugabannin suyi aiki tare domin ciyar da kungiyar gaba
Shima a nasa jawabin sabon zababben shugaban kungiyar ta NLC a jihar Katsina wanda aka zaba a karo na biyu, kwamred Hussaini Hamisu Yanduna ya godema yayan kungiyar bisa sake zabarshi a karo na biyu tare da basu tabbacin cigaba da aiki tukuru domin ciyar da kungiyar gaba
Kazalika ya nemi goyon bayan su domin samun nasara a sabon wa’adin da ya karba.
Leave a Reply