Take a fresh look at your lifestyle.

Karamar Sallah: Shugaba Tinubu Ya Isa Legas

44

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya isa Legas da sanyin safiyar Juma’a bayan wata ziyarar tarihi ta kwanaki biyu da ya kai kasar Burtaniya.

A gobe ne shugaban zai bi sahun sauran musulmi domin gudanar da bukukuwan karamar Sallah.

Shugaban kasar da uwargidansa, Oluremi Tinubu, sun sauka a filin jirgin saman Murtala Mohammed da ke Legas, da karfe 1:15 na safe.

Mataimakin gwamnan jihar Legas, Femi Hamzat, shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, uwargidan gwamnan, Dr. Claudiana Ibijoke Sanwo-Olu, da jiga-jigan jam’iyyar APC ne suka tarbe shi a bakin kwalta.

Da yake bayyana wani bangare na shirin Eid-el-Fitr na Shugaba Tinubu a Legas, wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Mista Bayo Onanuga ya fitar, ta bayyana cewa shugaban zai yi sallar idi a filin Sallar Idi na Barrack Dodan a safiyar Juma’a.

A cikin sakonsa na Sallah, Shugaba Tinubu ya bukaci Musulman Najeriya da su sadaukar da kansu ga kyawawan koyarwar watan mai alfarma, wanda ke jaddada tsoron Allah, tausayawa da hadin kai a tsakanin bil’adama.

Muna da abubuwa da yawa da za mu ciro daga darasin darussa na Ramadan, musamman a irin wannan lokaci, dole ne mu ci gaba da kiyaye kyawawan dabi’u na takawa, rashin son kai, dagewa, kyautatawa da jin kai bayan wannan lokaci,” inji shi.

Kafin tashinsa daga Landan, shugaba Tinubu ya gana da firaministan Burtaniya Sir Keir Starmer a Downing Street, inda kasashen biyu suka amince da yarjejeniyar sake gyara wasu manyan tashoshin jiragen ruwa guda biyu a Legas, da darajarsu ta kai fam miliyan 746.

Shugaban ya bayyana ziyarar aiki da ya kai kasar Birtaniya, wadda ita ce ta farko da wani shugaban Najeriya ya kai a cikin shekaru 37, a matsayin mai matukar farin ciki da kuma muhimmanci wajen karfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

“Ba za mu manta da ci gaban hukumomin da muka samu tsawon shekaru ba,” in ji shugaban na Najeriya a Downing Street gabanin tattaunawar da kasashen biyu ke yi.

Ya lura cewa tattaunawar ta shafi kasuwanci, tattalin arziki, sauyin yanayi, ta’addanci, da manyan kalubalen duniya.

Mai Martaba Sarki Charles na Uku ne ya karbi bakoncin Shugaba Tinubu da uwargidansa a wani liyafa da aka yi a Windsor Castle, inda ya ce Najeriya da Ingila sun yi tarayya fiye da tarihi.

Al’ummominmu biyu suna da hangen nesa na ci gaba da juriya. A yau, muna ci gaba da wannan tafiya, mun himmatu wajen samar da makoma mai tushe a cikin kawance, mutunta juna, da kyawawan dabi’u.”

Sarki Charles III da Sarauniya Camilla tun da farko sun karbi Shugaban kasa da Uwargidan Shugaban Kasa a Quadrangle a Windsor Castle. Shugaba Tinubu ya yi bitar mai gadin kuma an yi masa gaisuwar bindigu 42 daga hannun Sojojin dawakin Sarki.

 

Comments are closed.