Take a fresh look at your lifestyle.

Ranar Hijabi Ta Duniya: Uwargidan Shugaban Najeriya Ta Karrama Mata Musulmi, ‘Yancin Addini

506

Yayin da Najeriya ta bi sahun sauran kasashen duniya wajen bikin ranar hijabi ta duniya, uwargidan shugaban kasar, Oluremi Tinubu, ta ce tana mutunta zabin ‘yan kasar na imani ko addini.

A cikin sakon tunawa da ranar, Misis Tinubu ta yabawa matan musulmi bisa yadda suka nuna irin salon suturar da babu kamarta.

Uwargidan shugaban kasar ta ce ya kamata kowa ya amince da bambancin al’ummar kasar a matsayin tushen hadin kan ‘yan Najeriya. Ta ce:

“A wannan ranar Hijabi ta Duniya  2026, mai taken, ‘Haɗin kai a Hijabi,’ ina murnar zaɓe, imani, da kuma asalin mata Musulmi.

“Hijabi alama ce ta biyayya, daraja, ƙarfi, da kuma ibada ga mata da yawa, kuma abin tunatarwa ne cewa bambancin mu shine tushen haɗin kai, ba rarraba ba.”

Uwargidan shugaban kasar ta bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da mutunta addinin juna tare da rungumar zaman lafiya domin ci gaban kasa.

Ta kara da cewa, “A matsayinmu na al’umma, mu ci gaba da rungumar mutunta juna, zaman lafiya, da hadin kai a dukkan al’adu da imani, tare, mun fi karfi.

 

Aisha. Yahaya, Lagos

 

 

Comments are closed.