Isra’ila ta ce za ta kakaba wa zirin Gaza “cikakkiyar katanga”, gami da hana shigar da abinci da man fetur, a daidai lokacin da ake kara nuna alamun yiwuwar kai farmaki a kasa.
Jami’an kiwon lafiya a yankin da aka yiwa kawanya sun ce harin da jiragen Isra’ila suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama kuma suka jikkata.
Kwamishinan Tarayyar Turai Oliver Varhelyi ya ce kungiyar ta dakatar da “dukkan kudaden da ake biyan Falasdinawa nan take”.
Adadin wadanda suka mutu na baya-bayan nan ya kai Falasdinawa 560 a Gaza, a cewar Jami’an lafiya.
Harin ba-zata da Hamas ta kai a ranar Asabar ya zo ne bayan da Isra’ilawa ‘yan kawanya suka kai farmaki a harabar masallacin Al-Aqsa a ‘yan kwanakin nan kuma Isra’ila ta kashe Falasdinawa da dama a ‘yan watannin nan.
ALJAZEERA/ Ladan Nasidi.
I’m impressed, I have to admit. Seldom do I encounter a blog that’s both educative and engaging, and let me tell you, you’ve
hit the nail on the head. The problem is something
which too few people are speaking intelligently about. Now i’m very
happy that I came across this in my search for something relating to this.