Ministan Muhalli na Najeriya Mista Balarabe Lawal ya tabbatar wa Cibiyar Sabis ta Kimiyya ta Afirka ta Yamma kan Sauyin yanayi da Amfani da Kasa (WASCAL) na kudirin gwamnati na hada kai da Cibiyar don inganta karfin ‘yan Najeriya kan sauyin yanayi da canjin makamashi.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar WASCAL karkashin jagorancin Daraktanta Dokta Emmanuel Wendsongre Rande a wata ziyarar aiki da suka kai ma’aikatar a Abuja babban birnin kasar.
Ministan ya bayyana aniyar gwamnati na ci gaba da ba da tallafi da hadin gwiwa da hada kai da WASCAL da sauran cibiyoyi a kokarinta na magance matsalolin sauyin yanayi a yankin yammacin Afirka da Najeriya.
Ya ce ma’aikatar za ta halarci taron kasa da kasa kan sauyin yanayi (ICCC) da za a yi a Najeriya da kuma taron ministoci kan sauyin yanayi a Guinea Conakry a karshen wannan shekara.
Ministan ya yi amfani da dandalin wajen godewa gwamnatin Jamus bisa tallafin da hukumar WASCAL ke yi a yankin da kuma tabbatar da ingantaccen sauyin yanayi da samar da makamashi a yammacin Afirka.
Ya kuma yabawa WASCAL bisa yadda ta yi amfani da Jami’o’in Najeriya guda biyu wato Jami’ar Fasaha ta Tarayya ta Minna Jihar Neja da Jami’ar Fasaha ta Tarayya ta Akure a Jihar Ondo wajen bayar da tallafin karatu ga Daliban Nijeriya don yin karatu da bincike kan batutuwan da suka shafi yanayi a Nijeriya.
A jawabinsa na bude taron babban daraktan cibiyar kula da sauyin yanayi da kuma amfani da kasa (WASCAL) na yammacin Afirka Farfesa Emmanuel Ramde ya bayyana cewa kungiyar tasu ta samar da kwararru kan sauyin yanayi sama da 60,000 da suka samu digiri na farko da Masters da Ph.D.
Ya yi nuni da cewa shirye-shiryen nasu sun kuma hada da aikin bincike kan illar sauyin yanayi wajen samar da taki da ma’adinai da noma da dai sauransu.
Mista Ramde ya nemi goyon bayan ma’aikatar wajen karbar bakuncin taron kasa da kasa kan sauyin yanayi a Najeriya da taron ministoci kan sauyin yanayi a birnin Conakry na kasar Guinea.
Ladan Nasidi.