Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaban kasa Tinubu Ya Gana Da Sabbin Shugabannin Ma’aikata Da Aka Nada

42

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da sabbin shugabannin ma’aikata da aka nada a fadar gwamnati da ke Abuja, a ci gaba da kokarin karfafa gine-ginen tsaron Najeriya.

Shugabannin ma’aikatan sun halarci zaman sirri ne biyo bayan nadin da aka yi musu kwanan nan, wanda fadar shugaban kasar ta bayyana a matsayin wani shiri na inganta kwarewa, da sabunta kwarjini a cikin rundunar soji.

Wadanda suka halarci taron da shugaban kasar sun hada da babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Babban Hafsan Sojin kasa, Manjo Janar Waheedi Shaibu; hafsan hafsoshin sojin sama Air Vice Marshall Kennedy Aneke, da Rear Admiral Idi Abbas, babban hafsan sojin ruwa.

Har yanzu dai ba a bayyana cikakken bayani kan tuhume-tuhumen da shugaban kasar ya yi wa sabbin shugabannin sojojin ba.

 

Aisha. Yahaya, Lagos

Comments are closed.