Take a fresh look at your lifestyle.

‘Yan Jarida su Nemo Hanyoyin Dakile Labarun Karya da ake Yadawa

TIJJANI USMAN BELLO

0 140

Kwamishinan yada labarai, al’adu da al’amuran cikin gida, na jihar

Borno, Baba Kura Abba Jato, ya fadi hakan a lokacin da yake jawabi a

wajen taron karawa juna sani na kwanaki 2, mai taken ‘’Sanin hanyoyin

da Dan Jarida zai kare kansa daga rikice-rikice’’ wanda Kungiyar ‘Yan

Jarida ta (NUJ) ta Kasa reshen jihar Borno ta shirya, a garin

Maiduguri, bubban birnin jihar Borno.

 

 

 

Kwamishinan Baba Kura Abba Jato, ya lura cewar ‘’Akasarin labaran

da suke fitowa daga wasu sassan Kasarnnan labaraine na kanzon

Kuregene, kuma labaraine wadanda suke tayar da husuma a kasa ta yadda

rikicin Kabilancin Kabila, ko Bangaranci, Siyasa da na Addini ke

tasiri, kuma wannan duk ya samo asaline a watsa labaran karya a

wadannan kafafe, to adon haka nike kira ga ku ‘Yan Jarida ku lalubo

wadansu hanyoyi wanda zai rika karyata wadannan kafafe ta yadda za’a

sami dawawwamammen zaman lafiya a Kasa.’’

 

 

 

A kasidar da ya gabatar mai taken ‘’Canza Tsarin aikin Jarida da

shi kanshi Dan Jarida,’’ Shehin Malami mai Koyar da aikin Jarida a

Tsangayar koyon aikin Jarida ta Jami’ar Maiduguri, Farfesa Danjuma

Gambo, ya ce’’ A yanzu lokaci ya yi da ‘Yan Jarida zasu sauya akalan

labaransu daga rubuta labarun  kashe- kashe, ya zuwa labaun zaman

lafiya da ci gaban tattalin arziki, ganin cewar a yanzu haka an sami

cikakken zaman lafiya da walwala a daukacin jihar Borno dama wannan

Yanki na Arewa maso gabashi, sa’annan gwamntin jihar Borno ta dukufa

ka’in da na’in wajen gudanar da ayyukan raya Kasa.’’

 

 

 

 

Tun da farko sai da Shugaban Kungiyar ‘Yan Jarida ta Kasa reshen

jihar Borno, Malam Dauda Iliya, ya ce’’Kungiyar ta NUJ a jihar, ta

shirya wannan taron karawa juna sanine, saboda kokarin fahimtarwa tare

da wayar da kan  mambobinta a dangane da sauke nauyin da ya kamata su

sauke na fadakarwa, gami da ilimantar da alumman jihar a dangane da

abin da ya shafi zamantakewa a tsakanisu.’’

 

 

 

 

Ya ce’’Kungiyar har ila yau a karkashin jagorancinmu, ta kuduri

aniyar kyautata rayuwa gami da jin Dadin mambobinta a ko da wani

lokaci, fadakarwa tare da tunasar da mambbobi ta fuskar gudanar da

ayyuka a duk in da suka samu kawunansu, ta yadda zasu sami saukin

gudanar da ayyuka.’’

 

 

 

Malam Yakubu Musa wakilin Kamfanin Dillacin Labarune ta NAN, na

daya daga cikin wadanda suka halarci taron karawa juna ilimin, ya fada

cewar’’Wannan taron karawa juna ilimi wanda Kungiyar NUJ ta Borno ta

shirya abune wanda ya zo dai-dai a kan gaba domin kuwa babu ko shakka

na karu kwarai da gaske ta fuskar gudanar da ayyukana, tare kuma da

yadda zan kare kaina a yayin da na samu kaina a cikin wani kangi,

domin masana sun gabatar da kasidu daban-daban tare da kawo misalai na

yadda zamu iya gudanar da ayyukanmu a ko da wani lokaci.’’in jishi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *