Take a fresh look at your lifestyle.

Wani Kwale-kwale Ya Kife Daga Kasar Madagascar A Hanyar Zuwa Mayotte

Maimuna Kassim Tukur,Abuja.

0 198

Hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Madagascar ta sanar a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da wani jirgin ruwa dauke da su ya kife a tsibirin Mayotte na kasar Faransa, inda mutane 22 suka mutu.

 

 

Hukumar  ta sanar da cewa jirgin mai dauke da mutane 47 ya kife ne a ranar Asabar a tekun Ankazomborona da ke arewacin kasar Madagascar.

 

 

Hukumar ta ce kwale-kwalen ya yi hatsari, bayan da aka ceto 23 daga cikin wadanda ke cikin jirgin, yayin da aka gano gawarwaki 22.

 

 

Sauran biyun kuma ba a ji duriyarsu ba.

 

 

Wani dan sanda da bai so a bayyana sunansa ba ya ce akasarin wadanda aka ceto sun gudu ne don gudun kada a kama su saboda yunkurin tafiya zuwa Mayotte.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *