Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaba Buhari ya rantsar da sabbin sakatarorin dindindin guda shida

0 217

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da sabbin sakatarorin dindindin guda shida da aka nada.

 

An gudanar da bikin rantsarwar ne a safiyar ranar Laraba a zauren majalisar da ke fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja.

 

Wadanda aka rantsar sune; Adam Kambari daga jihar Borno, Esuabana Asanye, jihar Kuros Riba; Lamuwa Adamu Ibrahim, Jihar Gwambe; Yakubu Adamu, Jihar Kano; Oloruntola Micheal, Jihar Ogun; da Richard Pheelangwah, Jihar Taraba.

Bikin ya gudana ne gabanin taron mako-mako na Majalisar Zartaswa da ke gudana yanzu haka a zauren majalisar da ke fadar shugaban kasa ta Villa Abuja.

 

Wadanda suka halarci taron sun hada da sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha; Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan; da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya.

 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da ministar kudi, kasafin kudi, da tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed; Babban Lauya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami; da na Babban Birnin Tarayya (FCT), Mohammed Musa Bello, da sauransu.

 

A zantawar ta da manema labarai na fadar gwamnatin jihar, shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dakta Folashade Yemi-Esan ta bukaci sabbin sakatarorin dindindin da su bayar da dukkan gudunmawar su wajen gudanar da ayyukansu.

 

 

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *