Take a fresh look at your lifestyle.

Nijar: Jamus za ta shiga aikin soja na EU

0 235

Majalisar dokokin Jamus ta ba da haske kan batun tura sojoji Nijar.

 

Sojojin Jamus 60 ne za su shiga tawagar Tarayyar Turai da aka kafa a watan Disambar da ya gabata da nufin taimakawa kasar wajen inganta kayan aiki da kayayyakin more rayuwa.

 

Matakin da majalisar dokokin kasar ta dauka a birnin Berlin na kara tabbatar da ci gaba da zaman Jamus a yankin Sahel duk da janyewar kasar daga Mali.

 

Nijar dai na fuskantar barazanar tashe-tashen hankula da ke kunno kai daga makwabciyarta Mali inda mayakan ke ci gaba da samun galaba bayan janyewar sojojin Faransa da na wasu kasashen Turai.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *