Take a fresh look at your lifestyle.

Zimbabwe Zata Sake Daidaita Kudin ta

0 135

Zimbabwe na sake yin wani yunƙuri na daidaita kuɗinta da ke cikin “matsin lamba”, tare da hauhawar farashin dalar Amurka, a cewar shugaban kuɗin ƙasar.

 

 

Gwamnati ta ba da sanarwar cewa, daga ranar 15 ga Mayu, za a ba wa ‘yan kasuwa damar adana duk kudaden kasashen waje da aka samu daga tallace-tallacen cikin gida.

 

 

A baya, babban bankin ya bukaci a canza kashi 15% na tallace-tallacen dalar Amurka zuwa kudin gida ta hanyar amfani da kudin hukuma.

 

 

Babban bankin kuma zai kara yawan kudin ruwa wanda ya riga ya kasance mafi girma a duniya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *