π¬π¨π‘ππ¨π₯ππ‘ ππ‘π¨πͺππ₯ π π¨π¦π¨ππ ππ‘ π‘ππππ₯ππ¬π π‘π πππͺπ’ πππ₯π¦πππ‘ πππ¦πππ‘ πͺππ¬π π πππ‘π’
Yusuf Bala Nayaya,Kano.
Inuwar Musulman Najeriya da hadin gwiwar jamiβar Al-Istiqama da Kungiyar Dalibai Musulmai a Najeriya reshen jihar Kano sun gudanar da taro da ya yi tattaunawa ta musamman a kan annobar kwacen waya ko fashin wayoyin hannu a tsakanin alβumma. Matsalar da alβumma ke ganin ta gawurta.
Taron dai ya samu halartar kwararru a fannin ilimin tsaro da manazarta kan aikata miyagun laifuka da masu yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da jamiβan leken asiri da masu rike da sarautun gargajiya da malaman addini dana boko da ma masana kan halayyar dan Adam, baya ga sauran fannoni.Β Alhaji Gidado Mukhtar shi ya jagoranci taron wanda Farfesa Salisu Shehu sakataren zartarwa na Inuwar Musulman Najeriya ya bayyana makasudinsa da zama “Tattaunawa ta musamman akan annobar kwacen waya “a kokari na neman mafita ga annobar da a cikin kankanin lokaci dalilinta aka kama daruruwan matasa, abin da ke zama babbar barazana ga zamantakewar alβummar jihar Kano.
A cewar Farfesa Salisu Shehu fuska biyu za a iya kawo karshen matsalar fashin na waya; na daya ta hanyar amfani da karfi na jamiβan tsaro, sannan na biyu a zauna a yi nazari kan matsalar a gano sabubbanta a yi mafani da hankali da nasiha da canza tunani da dabiβar alβumma a dora alβumma kan turba mai kyau.
Dakta Maikano Madaki kwarraren masani kan ilimin aikata laifuka daga jamiβar Bayero ya gabatar da dogon jawabi kan abin da ake kira kwacen waya da yace tun daga Birtaniya shekaru kusan goma da suka gabata ake samun wannan dabiβa tsakanin matasa wadanda ba a raba su da shan miyagun kwayoyi, kuma abin takaici irin wayoyin da aka sata a can ana kawo su Najeriya musamman birnin Legas. Wannan dabiβa matasa a Najeriya su ma sun koya abin da ya kazanta kawo yanzu duk da kokari na jamiβan tsaro. Hakan ya sa ake ganin jamiβan tsaron na bukatar a kara masu yawa da kayan aiki irin na zamani, alβumma kuma su ci gaba daΒ ba su hadin kai, sannan a bawa matasa kulawa da ta dace.
A bangaren kwamishinan βyansanda na jihar Kano kuwa Usaini Gumel da ya samu wakiltar jamiβi da ke magana da yawun βyansanda na jihar ta Kano PPRO SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce wannan matsala ta kwacen waya ba karama ba ce don haka suke aiki ba dare ba rana, kuma sannu a hankali saboda hadin kai da suke samu na alβumma suna samun nasara. Sai dai Kiyawa ya ja hankali na alβumma su guji daukar doka a hannu kasancewar hakan baya samar da mafita duba da yadda a Kudanci Najeriya yadda wasu ke daukar doka a hannu hakan bai samar da mafita ba, ana ci gaba da samun masu aikata laifuka.
A nasa tsokaci fitaccen malamin addinin Islama a Kano Malam Aminu Daurawa ya ce βMuddin a na so a kawo karshen kwacen waya sai alβumma ta amince cewa hakkin tarbiya abu ne da ya rataya a wuyan kowa a tallafa wa marasa galihu da marayu a taimaki zawarawa a samar wa matasa abin yi, uwa uba a samar da zauren sulhu da zai rika duba matsalolin tsaron alβumma tun daga matakin unguwanni don daidaita matsaloli na zamantakewa kafin ma zuwa ga βyansanda .
Shima a nasa tsokaci Alhaji Ilyasu Muβazu Sharada dagacin Sharada a jihar ta Kano ya bayyana cewa dole a rungumi matasa a kula da rayuwarsu sai an koma dabiβar nan ta cewa da na kowa ne sannan za a ga daidai.
Muhammad Salisu Kabir shugaban kungiyar Musulman Najeriya reshen jihar Kano ya yi nasa tsokacin kan taron da cewa an samu masana da suka yi bayanai sosai kan matsalar satar wayar ta mahanga daban-daban, mataki na gaba shine a zauna don tattaunawa kan wadannan matsaloli da aka gano don daukar mataki na gaba, a fitar da shawarwari wanda za a mika wa hukuma a mika, wanda kuma za a ba wa kungiyoyi na alβumma a basu,Β suma alβumma a sanar da su abin da ya kamata su yi ko su sani, duk dai don a samu mafita ga wannan matsala ta satar waya da sauran matsaloli don samun zamantakewa mai nagarta.
Uban taron kuma wakilin Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, DanβAmar na Kano Aliyu Harazumi Umar a nasa jawabin a wajen taron ya jadda muhimmanci na rawar da masu sarautar gargajiya za su taka muddin ana son shawo kan irin wannan matsala ta fashin waya dama dangoginta kasancewar irin masu wannan sarauta su suka fi kusanci da jamaβa.
Da dama cikin wadanda suka halarci taron da aka yi a shelkwatar ta Inuwar Musulman Najeriya da ke a Farm Centre a Kano sun nunar da cewa taro irin wannan da zai tattara kwararru a fannin Β tsaro da sauran masu ruwa da tsaki, ba kawai zai ba da mafita ga matsalar ta fashin waya ba har ma da wasu matsaloli na zamantakewa.
Excellent content! I completely agree with your points.
Looking forward to more