Take a fresh look at your lifestyle.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da zabtarewar kasa sun kashe mutane akalla 10

0 243

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da zaftarewar kasa a babban birnin kasar Ivory Coast, Abidjan, ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 10, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

 

Tara sun kasance a gundumar Yopougon kuma ɗayan yana Cocody-Angre, shugaban hukumar kashe gobara ta soji (GPSM) ya ce.

 

Zabtarewar kasa biyu a Yopougon da sanyin safiyar Alhamis ta yi sanadiyar mutuwar wasu da jikkata wasu da dama.

 

A Cocody-Angre wani ya nutse bayan “ruwa ya tafi da shi”, Anicet Bah, kyaftin din GSPM kuma mataimakin shugaban ayyuka,

 

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ba sabon abu ba ne a wannan lokaci a Abidjan, sai dai kamfanin dillancin labaran AFP ya ce a yayin da birnin ke bunkasa gine-ginen ya zama cikin hadari musamman a gundumomin da ba su da wadata.

 

 

BBC/L.N

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *