Take a fresh look at your lifestyle.

Ecowas ta ki amincewa da shirin mika mulki na shekaru uku a Nijar

0 99

Kungiyar kasashen yammacin Afirka, Ecowas, ta yi watsi da sanarwar da jagoran juyin mulkin Nijar ya yi cewa ba za a iya maido da mulkin farar hula ba har tsawon shekaru uku.

 

Kwamishinan harkokin siyasa na kungiyar, Abdel-Fatau Musa, ya ce ba za a amince da jadawalin ba.

 

A ranar Asabar din da ta gabata, Janar Abdourahamane Tchiani ya ce ana bukatar tattaunawa ta kasa domin kafa harsashen sabon tsarin siyasa a Nijar.

 

Kungiyar Ecowas ta yi barazanar daukar matakin soji don dawo da hambararren shugaban kasar.

 

Jama’a sun sake yin gangami a Yamai babban birnin kasar, domin nuna goyon bayansu ga juyin mulkin.

 

Sai dai rahotanni sun ce wasu da ke adawa da mamayar sojojin na fargabar bayyana ra’ayoyinsu a bainar jama’a

 

 

BBC/Ladan Nasidi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *