Take a fresh look at your lifestyle.

Erdogan Zai Gana Da Shugaban Kasar Azarbaijan Yayin Da Dubban Mutane Ke Kaura Daga Karabakh

1 306

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan zai gana da abokin karawarsa Ilham Aliyev a ranar Litinin, yayin da dubban ‘yan kabilar Armeniya suka tsere daga Nagorno-Karabakh bayan da Azarbaijan ta fatattaki mayakan yankin a makon jiya.

 

Erdoğan zai kai ziyarar kwana guda a Nakhchivan na Azarbaijan mai cin gashin kan shi, wani yanki na Azeri da ke tsakanin Armenia, Iran da Turkiyya domin tattauna wa da Aliyev halin da ake ciki a yankin Karabakh, in ji ofishin shugaban Turkiyya.

 

Armeniyawa na Karabakh, yankin da duniya ta amince da shi a matsayin wani bangare na Azarbaijan amma a baya ya wuce ikonsa, an tilastawa tsagaita bude wuta a makon da ya gabata bayan wani samamen da sojojin Azabaijan suka yi na tsawon sa’o’i 24.

 

A ranar Lahadin da ta gabata, shugabannin Nagorno-Karabakh sun ce Armeniyawa 120,000 na yankin ba sa son zama a matsayin wani bangare na Azarbaijan saboda tsoron tsanantawa da kawar da kabilanci suka fara ficewa daga yankin.

 

Tun da misalin karfe 5 na safe (0100 agogon GMT) a ranar Litinin, sama da mutane 2,900 ne suka tsallaka zuwa Armenia daga Nagorno-Karabakh, in ji gwamnatin Armeniya a cikin wata sanarwa.

 

 

 

REUTERS/ Ladan Nasidi.

One response to “Erdogan Zai Gana Da Shugaban Kasar Azarbaijan Yayin Da Dubban Mutane Ke Kaura Daga Karabakh”

  1. fantastic publish, very informative. I’m wondering why the other specialists of this sector do not understand this. You should proceed your writing. I am sure, you’ve a great readers’ base already!

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *