Take a fresh look at your lifestyle.

Ukraine: Adadin Wadanda Suka Mutu A Hroza Ya Kai 52, A Binciken Majalisar Dinkin Duniya

0 169

Adadin wadanda suka mutu sakamakon harin da jirgin saman da aka kai a kauyen Hroza da ke Arewa maso Gabashin kasar Ukraine ya karu zuwa 52 a ranar Juma’a yayin da masu aikin ceto ke lekawa baraguzan gawarwaki bayan da Kyiv ya ce yana daya daga cikin hare-hare mafi muni da Moscow ta kai kan fararen hula tun bayan mamayar ta.

 

Gwamnan yankin ya ce mutumin na baya-bayan nan ya mutu ne da daddare a asibiti, biyo bayan harin da makami mai linzami ya fada a wani wurin sha da shaguna a ranar Alhamis yayin da jama’a suka taru domin alhinin wani sojan Ukraine da ya mutu.

 

“Mutane 52 ne suka mutu sakamakon harin makami mai linzami. Mutum daya ya mutu a wani wurin jinya,” Oleh Synehubov, gwamnan yankin Kharkiv, ya ce.

 

“Mutane na can (a asibitoci). Raunin yana da muni sosai.”

 

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi Allah wadai da harin makami mai linzami, in ji kakakin MDD, yana mai cewa “an haramta kai hare-hare kan fararen hula da ababen more rayuwa a karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa”.

 

A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai hukumar kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta tura tawagar da za ta binciki harin, in ji kakakin OHCHR a birnin Geneva.

 

 

 

REUTERS/ Ladan Nasidi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *