Take a fresh look at your lifestyle.

Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Ana Tursasa Gaza A Cikin Wani Rami Mai Zurfi

0 120

Harin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 2,450 tun bayan harin da Hamas ta kai a kudancin Isra’ila a makon jiya, in ji ma’aikatar lafiya ta Gaza.

 

Ma’aikatar ta kara da cewa wasu mutane 9,200 kuma sun jikkata yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare ta sama a kan yankunan da ke gabar tekun Falasdinu.

 

Hukumar ba da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ta shaida wa BBC cewa “ana tura Gaza cikin wani rami mai zurfi.”

 

Iran a ranar Lahadi ta yi gargadin cewa duk wani farmakin kasa da Isra’ila za ta kai a zirin Gaza zai iya fadada yakin da ake yi a wasu wurare a Gabas ta Tsakiya.

 

 

BBC/ Ladan Nasidi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *