Take a fresh look at your lifestyle.

Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Sauke Shugabannin Kananan Hukumomi

Binta Aliyu ,Kebbi.

163

Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya Sauke shugabanin kananan hukumomi da sakatarorin su,biyo bayan kammala wa’adin mulkin su, na shekara biyu.

 

Kwamishinan Kananan hukumomi da lamuran masarautu a jihar, Alhaji Abubakar Garba Dutsin Mari shine ya bayya na hakan ga yan- jaridu a fadar Gwamnatin dake Birnin Kebbi.

 

Kwamishinan Kananan hukumomi da lamuran masarautu, Alhaji Abubakar Garba Dutsin Mari yace akasarin sakatarorin kananan hukumomin ‘yan-siyasa ne, hakan yasa, za’a mika wa, Daraktan kula da ma’aikata mulkin kananan hukumomin.

 

Kwamishinan, yace Gwamnatin Jihar zata gudanar da zaben kananan hukumomin nan bada jimawa ba.

 

 

Binta Aliyu.

Comments are closed.