Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaba Buhari Ya Baiwa Dr. Malami Lambar Yabo Ta (MFR)

Abdulkarim Rabiu, Abuja

0 274

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da ba wa Dr. Malami Shehu Ma’aji Lambar Yabo ta kasa (MFR).

Hakan na kunshe ne a wata takarda da ministan ayyuka na musamman da harkokin gwamnati, Mista George Akume ya sanyawa hannu kuma ya aikewa Dr. Malami.

A wasikar mai lamba: FMSDIGA/NHA/001/93, Ministan ya ce: “Ina farin cikin sanar da kai cewa, Shugaban Tarayyar Najeriya, Mai Girma Muhammadu Buhari, GCFR, ya amince a baka lambar yabo ta kasa ta Karramawa a matsayin MFR (Member of Order of the Federal Republic)”.

A cewar Ministan, za a gudanar da bikin bada lambar yabon ne a cibiyar taron kasa da kasa da ke Abuja a ranar 11 ga watan Oktoba, 2022.

Akume ya Kuma taya Dr Shehu Malami murnar karramawar kasa a matsayin MFR.

 

AK

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *