Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaba Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Marigayi Gwamna Akeredolu

92

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu.

 

Shugaba Tinubu ya ziyarci iyalan marigayi Akeredolu a Owo, jihar Ondo, kwanaki bayan an binne tsohon gwamnan.

 

Shugaba Tinubu ya ce za a yi wuya a cike gurbin da gwamnan ya bari, yana mai jaddada cewa “gadonsa za su dawwama har abada.”

“Ya nuna jarumtaka da rashin tsoro, musamman a kokarinsa na neman shugabanci nagari. Ya kasance mai ba da shawara marar tsoro, mai sadaukar da kai ga jin daɗin jama’arsa. Za a rika tunawa da jajircewarsa a koyaushe,” in ji Shugaban.

 

Tsohon gwamnan ya rasu ne bayan ya yi fama da cutar kansar prostate da kuma cutar sankarar jini a ranar 27 ga Disamba, 2023, yana da shekaru 67 a duniya.

 

Shugaban na Najeriya ya kuma ziyarci Pa Reuben Fasoranti, shugaban kungiyar Afenifere ta kabilar Yarabawa.

 

 

Ladan Nasidi.

Comments are closed.