Take a fresh look at your lifestyle.

Gwamnatin Najeriya Ta Saka Tsohon Gwamnan Kogi A Jerin Wajen Sa ido

187

Gwamnatin Najeriya ta sanya tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a cikin jerin sunayen ta na sa ido, inda ta sanar da Hukumomin Taro a kasar da kuma Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya NIS da su kama shi a duk lokacin da zai fita.

Shugaban hukumar kula da shige-da-fice ta kasa, Kemi Nanna Nandap ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta aikewa hukumomin tsaro a kasar.

Takardar mai dauke da sa hannun ACI DS Umar ta bayar da cikakkun bayanan fasfo na kasa da kasa na tsohon gwamnan.

An umurce ni da in sanar da ku cewa an sanya wanda aka ambata a sama a jerin masu kallo.

“Ya isa a ambaci cewa ana tuhumar wannan batu a gaban babbar kotun tarayya Abuja bisa laifin hada baki, karya amana da kuma karkatar da kudade ta hanyar bidiyo mai suna Ref; CR; 3000/EFCC/LS/EGCS.1/TE/V1/279 mai kwanan wata 18 ga Afrilu 2024. Idan an gan shi a wurin shiga ko fita, sai a kama shi a mika shi ga Daraktan Bincike ko a tuntubi 08036226329/07039617304 don ci gaba da daukar mataki.

“Don Allah a yarda kamar yadda ko da yaushe Babban Kwanturola Janar na gaisuwa da girmamawa”. Memo ya karanta a sashi

A wani labarin kuma, Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya IGP Olukayode Egbetokun ya janye jami’an ‘yan sandan da aka baiwa Yahaya Bello.

Idan dai ba a manta ba a ranar Alhamis ne Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta bayyana tsohon Gwamnan Jihar Kogi da laifin cin hanci da rashawa.

Hukumar EFCC na neman tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, bisa laifukan da suka shafi tattalin arziki da kudi har naira biliyan 80.2.

“Duk wanda ke da labarin inda yake to ya kai rahoto ga hukumar ko kuma ofishin ‘yan sanda mafi kusa.”

 

Comments are closed.