Take a fresh look at your lifestyle.

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kan Ziyarar Aiki Zuwa Jihar Taraba

308

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya isa Jalingo babban birnin Jihar Taraba  a wata ziyarar aiki a jihar.

Mataimakin shugaban kasa ya sauka a filin jirgin saman Danbaba Suntai dake Jalingo da misalin karfe 9:17 agogon GMT

VP Shettima ya samu tarbi daga gwamnan Jihar Kefas Agbu da mambobin majalisar zartarwa ta Jihar Taraba

Jim kadan bayan isowar  mataimakin shugaban kasar ya karzaya  inda zai kaddamar da filin jirgin saman Danbaba Suntai da aka gyara a Jihar.

Daga nan ne ya ci gaba da kaddamar da sabon dakin liyafa da aka gina a harabar gidan gwamnati Jalingo.

Haka kuma zai bude wani dandalin zuba jari na kasa da kasa a Taraba karon na farko 2025.

Aisha.Yahaya, Lagos

Comments are closed.