Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaban Namibiya Ya Karbi Ragamar Manyan Ma’aikatu

29

 

Shugaban kasar Namibiya Netumbo Nandi-Ndaitwah ya sauke Natangwe Ithete daga mukaminsa na mataimakin firaminista kuma ministan masana’antu, ma’adinai da makamashi, fadar shugaban kasar ta bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.

“Don tabbatar da ci gaba da ingantaccen aiki a cikin wannan muhimmin bangare, Shugaba Nandi-Ndaitwah zai dauki nauyin Ma’aikatar Masana’antu, Ma’adinai da Makamashi, nan da nan,” in ji sanarwar.

Bai Bada Dalili Ba.

An nada Itthete kan mukaman a watan Maris a matsayin wani bangare na sabuwar gwamnatin Nandi-Ndaitwah. Ya ci gaba da zama Dan majalisa, in ji sanarwar.

Namibiya na shirin hako danyen mai na farko a shekarar 2030 bayan wasu manyan bincike da aka yi a shekarun baya-bayan nan. Yana hako kayayyaki kamar uranium da lu’u-lu’u.

 

Reuters/Aisha.Yahaya, Lagos

Comments are closed.