Take a fresh look at your lifestyle.

Kungiyar Gwamnonin Najeriya Sun Taya Gwamnan Anambra Murnar Sake Zabensa

10

Kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) ta mika sakon taya murna ga gwamna Chukwuma Soludo kan nasarar da ya samu a zaben gwamnan jihar Anambra da aka yi ranar Asabar da ta gabata.

Wata sanarwa dauke da sa hannun shugaban kungiyar wanda kuma shi ne gwamnan Jihar Kwara a ranar Lahadin da ta gabata, ta ce tazarar nasarar da aka samu ya nuna farin jinin gwamnan da shirye-shiryensa a tsakanin al’umma.

Yana karanta; “Muna da yakinin cewa wannan nasarar da ta dace za ta baiwa mai martaba damar karfafa manyan nasarorin da ya samu a bangarori daban-daban.

“Muna kuma taya al’ummar Anambra da duk masu ruwa da tsaki murnar gudanar da zaben cikin tsari da lumana – wata hujjar da ke nuna cewa ‘yan Najeriya sun rungumi tsarin dimokradiyya da bin doka da oda a matsayin zabin shugabanci.

Muna kuma yaba wa hukumar zabe mai zaman kanta da jami’an tsaro bisa yadda aka gudanar da zaben cikin tsari zuwa yanzu.”

 

Aisha. Yahaya, Lagos

Comments are closed.