Take a fresh look at your lifestyle.

Gwamnan Borno Ya kaddamar da Kasuwar Kasa da Kasa ta Dabbobi

TIJJANI USMAN BELLO, Maiduguri.

0 263

A lokacin da yake jawabi yayin bude wannan bubbar Kasuwar Kasa da

kasa ta Dabbobin a garin Gamboru a Yankin Karamar Hukumar Ngala, dake

da tazarar nisan kilo mita sama da 130, daga garin Maiduguri bubban

birnin jihar Borno, da kuma ya hade kan iyakansa da Jamhuriyar

Camaroun.

 

 

Gwamnan jihar Barno Babagana Umara  Zulum , ya ja kunnen daukacin ‘Yan

kasuwar dabbobin  da su guji tsunduma kansu a harka irin ta Boko

haram, ya ce’’ Duk wani Dan kasuwar Shanun da aka kama da hannu

dumu-dumu da wanda zai kai ga sake rufe kasuwar to ko zai dandanama

aya tsaki, a don haka ina horonku da ku guji aikata wasu munanan

dabi’u ku rike harkar kasuwancinku wanda zai iya kaimu ga habaka

tattalin arzin jihar dama Kasa baki daya.’’

 

 

Ya ce’’Bude wannan Kasuwa zai ci gaba da habaka tattalin arzikin

Kasa ganin cewar Kasuwace wacce ta hade Kasashen Camaroun zuwa Africa

ta Tsakiya, to kuma za muyi kokarin cewar an samar da kayayyaki don

habaka kiwo da noma ta yadda za’a iya fitar dasu Kasashen Makwabta.’’

 

 

Hakazalika ina rokonku da ku ci gaba da baiwa Jami’an tsaro cikakken

hadin kai da goyon baya ta yadda za’a sami nasarar fatattakar ayyukan

ta’addanci a kasa baki daya.

 

 

Tun da farko sai da Kwamandan Bataliya ta 3 ta Sojojin Najeriya

Laftanar Kanar Tolu Adedokun, ya tabbatar da samun cikakken tsaro a

yankun to amma sai ya ce’’ Duk Dan kasuwar Shanun da aka kamashi da

hannu dumu-dumu yana hada kai da ‘Yan ta’addan Boko haram to za’a

hukuntashi kamar yadda doka ta tanadar, to kuma a ta bangaremu zamu ci

gaba da iya kokarinmu wajen samar da cikakken zaman lafiya a wannan

Yanki saboda haka muna rokonku da ku ci gaba da bamu cikakken hadin

kai da goyon baya don samun nasarar kawar da ayyukan ta’addanci.’’

 

 

A jawabin godiya a madadin ‘Yan kasuwar, Shugaban ‘Yan

Kasuwar Shanun Alhaji Yakubu, ya ce’’Zamu yi iya kokarinmu wajen bin

doka da oda don tabbatar da samun zaman lafiya a wannan kasuwan da aka

bude yau, kuma har ila yau zamu ci gaba da baiwa Jami’an tsaro

cikakken hadin kai da goyon baya don magance ayyukan ta’addanci a

wannan kasuwa, domin kuwa kowa ya dandana kudanrsa kuma abin ya shafi

kowa a don haka zamu hada hannu da jami’an tsaro don samun ingantuwar

kasuwancin dabbobi a wannan yankin.’’.

 

 

 

A karshe gwamna Zulum, ya rarraba kayayyakin Abinci da Tufafi har na

Miliyoyin Nairori ga ‘Yan gudun hijiran da suka koma wannan garin na

Gamboru Ngala da wasu garuruwan da suka yi gudun hijiran.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *