Take a fresh look at your lifestyle.

Uganda ta musanta samun karuwar cutar Ebola da ke da alaka da gasar gudun Fanfalaki

Aisha Yahaya

0 295

Ma’aikatar lafiya ta Uganda ta musanta ikirarin cewa wani taron gudu da aka gudanar a karshen makon da ya gabata a Kampala babban birnin kasar, wani lamari ne mai yaduwa da cutar Ebola.

 

A cikin wata sanarwa da ta fitar, ma’aikatar ta ce babu wani mahaluki a gasar gudun marathon da ya gabatar da wata alama ta kwayar cutar mai saurin kisa. Ya kara da cewa babu wani mai dauke da cutar Ebola da aka yi rajista a babban birnin kasar fiye da wadanda aka kebe.

 

A halin da ake ciki, kasar na fama da bullar cutar Ebola da ya zuwa yanzu ta kashe mutane sama da 50. An rufe makarantu tare da sanya dokar hana fita a wasu gundumomi biyu da ake tunanin sune farkon barkewar cutar. Hukumomin kasar sun ce an yi kokarin hana fitar da cutar zuwa wasu sassan kasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *