Take a fresh look at your lifestyle.

Zan Bar Ofis A Shekara Mai Zuwa – Shugaban Najeriya Ya Tabbatar Wa ‘Yan Kasar

Aisha Yahaya

0 259

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a ranar Litinin din da ta gabata ya jaddada aniyarsa na mika ragamar mulki ga zababben shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayun shekara mai zuwa 2023,  yana mai cewa wa’adin mulkin sa zai kare a wannan rana kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

 

 

A wani takaitaccen jawabi ga Mista Shakib Ben Musa, Ministan Ilimi na Kasa, Makarantu da Wasanni na Masarautar Morocco wanda ya ziyarci fadar gwamnati a matsayin  manzon na musamman kare da bikin rantsar da sabon shugaban kasa a watan Mayun badi.

 

Sai dai ya ce zai yi nazari kan sakon da aka aiko tare da mayar da martani yadda ya kamata, tare da bayar da tabbacin a lokaci guda zai ci gaba da kula da karfafa kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

 

Wakilin Masarautar Morocco a Najeriya, Mista Moha Ou Ali Tagma, wakilin na musamman ya sake jaddadawa shugaban kasar zumunci da hadin kan Sarki da gwamnati da al’ummar kasar Moroko da ‘yan Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *