Take a fresh look at your lifestyle.

SASHIN KULA DA AL’AMURAN MATA TA UN TA BUKACI HADIN KAN MATA A NAJERIYA

TIJJANI USMAN BELLO, Maiduguri.

0 157

A lokacin da take jawabi a yayin bude taron karawa juna sani na

kwaniki biyu, da sashin kula da al’amuran Mata ta Majalisar Dinkin

Duniya UN da hadin gwiwar wasu Kungiyoyi suka shiryawa Mata ‘Yan

takarar Mukamai a  jam’iyyu daban-daban, da aka gudanar dashi a garin

Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno dake Arewa Maso gabashin

Najeriya.

 

Bubban Jami’a a sashin kula da hakkin Matar a Najeriya, Uwargida

Emmanuela Azu, ta ce,’’Samun hadin kan Mata a tsakaninsu yana daya

daga cikin samun nasarar Mace ta a halin Karatu, Siyasa, Aikin

Gwamnati da wasu al’amuran yau da kullum, a don haka wajibine ku hada

kawunanku ku zama tsintsiya madaurinki daya, da manufa daya, sannanne

zaku samu nasara tare da ci gaba.’’

 

Ta ce,’’ Ba muna cewa Mata su yi kafada da kafada da Mazabane, amma

dai muna kokarin fahimtar da Mutanene su fahimci irin taimakon da

Uwargida take yima Maigidane wajen tafiyar da harkokin gida,

musanmamma a tafiyar da rayuwar Yara, a don haka wajibine Mata su mike

tsaye wajen neman ilimi, tsunduma cikin siyasa, da neman Mukaman

gwamnati don taimakawa Iyalai, domin a wani lokacin Maigida zai iya

gajiyawa, to amma idan Mata tana da wani abinyi to zata iya taimakawa

gida.’’

 

A kasidar da ta gabatar a wajen taron Shehin Malama a Tsangayar

Kimiyyar Siyasa a Jami’ar Maiduguri Uwargida Patricia Donly, ta tabo

muhimmancin baiwa Mata taka rawa a fagen Siyasa,

 

‘’Baiwa Mata

dama su taka rawa a fagen Siyasa yana da muhimmanci matuka gaya, domin

zata iya cike gurbin daman da Mata suke samu a wasu wuraren, kuma zata

iya taimakawa Mata ‘yan uwanta da Maigida da Yara a cikin gida, a don

haka maganar ace a hanawa Mata rawar takawa a wannan zamanin abune

wanda yake da matsanancin wahala ga su kansu Matan, a don haka muna

kira ga alumma su fahimci abin da muke nufi na shigar da kashin Mata

cikin gwagwarmayar Siyasa ko ilimi, da sauran harkokin rayuwa.’’

 

Itama a kasidar da ta gabatar mai karfafawa Mata karfin gwiwa Malama

Maimuna Garba, Ma’aikaciya a Hukumar Gidan Talabijin ta Kasa NTA a

Maiduguri, ta ce ‘’Mata wajibine Mata ku cire tsoro, kuma kasance

masu kwarin gwiwa da kyakkyawar zato, sannan kuma ku cire kyashi da

bakin ciki a tsakaninku.’’

 

Ita ko ‘Yar takarar gwamna a karkashin tutar jam’iyyar ADC, Malama

Fatuma Abubakar, ‘’Na tsaya wannan takarane don in tsamar da

Matasanmu daga shiga munanan Dabi’u, in kuma yi kokarin samar da

aikinyi gas u kansu Matasan da suka kammala Makaranta, don dogaro da

kai, sannan kuma zan kafa kananan Masana’antu da inganta samar da

wutar lantarki, don inganta kananan Masana’antun, sannan kuma zanyi

kokarin inganta harkar ilimi da kiwon lafiya, in har na samu daman

darewa wannan kujera, in jita.

 

‘Yan takara daga mukamai daban-dabanne

a maban-banta jam’iyyune suka halarci taron karawa juna sanin da aka

gudanar dashi a garin Maidugurin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *