Take a fresh look at your lifestyle.

MATAIMAKIN SHUGABAN KASA Osinbajo YA JAGORANCI TARON MAJALISAR ZARTASWA

0 270

Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranci taron Majalisar Zartaswa a ranar Laraba.

Ana gudanar da taron Majalisar zartaswar ne a fadar Shugaban kasa dake,babban birnin tarayya, Abuja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron har da Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Hadimin Shugaban kasa, Farfesa. Ibrahim Gambari; da Sakataren din din din a gidan gwamnati, State House, Umar Tijani.

Ministocin da suka samu halatar taron Majalisar na ranar  laraba sun hada da na Kimiya da Fasaha, Ogbonnaya Onu; Harkokin Wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama; Yada labarai da al’adu, Lai Mohammed; Babban birnin tarayya Mohammed Bello, MakamashiMuazu Sambo; Masanaantu, Ciniki da saka Jari, Niyi Adebayo; da Wasanni da ci gaban Matasa, Sunday Dare.

Sauran wadanda suka halarci taron majalisar zartaswar akwai Ministan kasa na Maaikatar kimiya da Fasaha, Hassan Abdullahi; Makamashi Jedy Agba; da na aiyyuka da gidaje, Abubakar Aliyu.

Sauran Mambobin Majaliisar zartaswar sun samu halarta ta yanara Gizo daga ofisoshin su.

LADAN  NASIDI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *