Take a fresh look at your lifestyle.

Wata Ƙungiyar Ta Ƙaddamar Da Goyon Bayan Gwamna Makinde A Zaben Shugaban Ƙasa 2027

43

Wata kungiyar da ke kira ga gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo gabanin zaben shugaban kasa a 2027  kungiyar Brave New Vision Support Group ta bukaci goyon bayan ‘ya’yan jam’iyyar PDP na Kudu-maso-Yamma.

Babban jigon jam’iyyar PDP Dr. Adetokunbo Pearse  ya shaidawa manema labarai cewa  yankin dole ne ya tabbatar Makinde ya zama Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a 2027

Da yake kira ga sabon shugaban jam’iyyar PDP shiyyar Kudu-maso-Yamma karkashin jagorancin Alhaji Kamorudeen Ajisafe  Pearse ya ce aikin da ke gaban shugabannin jam’iyyar na shiyyar shi ne hada kai don ganin Makinde ya fito.

Babban manufar kowace jam’iyyar siyasa ita ce ta ci zabe domin ta aiwatar da manufofinta na inganta rayuwar al’umma.

“A wannan lokaci yayin da muke shiga zaben 2027 babban aikin da ke gaban Ajisafe da kwamitinsa shi ne hada kan ‘yan siyasar PDP na Kudu-maso-Yamma.

“Dole ne mu karfafa tsarinmu a shirye-shiryen samun nasarar zabe a dukkan matakan gwamnati.

“Makinde ya kasance mafi kyawun samfurinmu ga PDP a zaben shugaban kasa  a 2027.

Dole ne mu yi aiki don aiwatar da wannan aikin. Pearse ya ce “Dole ne yankin da za a gudanar da taron ya yi kasa a gwiwa tare da fara hada kai da kuma hada kan dukkan yankunan da ke goyon bayan Makinde don kwato talakawa,” in ji Pearse.

NAN/Aisha.Yahaya, Lagos

Comments are closed.