Take a fresh look at your lifestyle.

WASANNIN KASASHE RENON INGILA: SHUGABA BUHARI YA TAYA TAWAGAR NAJERIYA MURNA

0 373

A ranar Lahadi Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari ya taya ‘yan was an tseren da suka wakilci Najeriya a wasannin kasashe renon ingila da aka gudanar a birnin, Birmingham 2022.

Shugaban ya bi sahun sauran Miliyoyin ‘yan Najeriya masoya wasannin motsa jiki murnar rawar gani da suka nuna a gasar da kimanin ‘yan wasannin tsare dubu biyar  suka halarta daga kasashe 75, domin gasar lashe kyautuka 280.

Da yake jinjina wa tawagar ‘yan wasan tseren Najeriya,Shugaban ya yaba da irin rawar gani da ‘yan Najeriya 94 a matsayin sun a jakadai na gari da suka daga Tutar Najeriya a wasannin Tara,daga karshe aka karrama su da kyaututtuka tare da annuri a fuskokin su a lokacin da ake rataya musu.

LADAN NASIDI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *