Shugaban ‘yan sandan Najerioya (IGP) Usman Alkali Baba,ya bada umurnin karin Jami’an tsaro a Makarantu,Asibiti da dukiyoyi a fadin kasar.
Jami’in hulda da Jama’a na rundunar ‘yan sanda, Olumuyiwa Adejobi, ya sanar da haka a shafin sada zumunta na Twitter ranar Lahadi 14 ga watan Agusta, 2022.
Shugaban rundunar ‘yan sandan ya bada wannan umurni ne sakamakon rahotanni harkokin tsaro a fadin kasar.
*IGP ORDERS WATER-TIGHT SECURITY AROUND SCHOOLS, HOSPITALS, CRITICAL INFRASTRUCTURES*
*Directs Constant Visibility Policing Across Board* pic.twitter.com/YkJ7zcEukS
— Nigeria Police Force (@PoliceNG) August 14, 2022
“Hakazalika IGP ya kuma baiwa ‘yan sandan sintiri su rinka bincike da kame domin dakile duk wata hanyar aikata manyan laifuka a jihohi da Birane a duk faadin kasar.”
Yayi kira ga Jami’an tsaron su rinka tara bayanan sirri da kuma kama duk wanda ya aikata laifi ba bias doka da oda bad a kuma zakulo duk maboyar masu laifi.
LADAN NASIDI
Leave a Reply