Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaban Sojojin Mali Da Shugaban Kasar Rasha Sun Tattauna Kan Juyin Mulkin Nijar

0 131

Shugaban sojojin Mali, Assimi Goita, ya bayyana cewa kwanan nan ya tattauna ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin kan halin da ake ciki a Nijar.

 

Jamhuriyar Nijar dai ta fuskanci juyin mulkin da sojoji suka yi, lamarin da ya janyo damuwa a kasashen duniya.

 

A cikin wani sako da aka watsa a dandalin sada zumunta na X (tsohon Twitter), Goita ya bayyana cewa, Putin ya jaddada muhimmancin kudurin lumana don tabbatar da zaman lafiya a yankin Sahel.

 

Kasashen yammacin duniya na fargabar cewa Nijar na iya bin tafarkin Mali, inda a baya aka yi juyin mulkin da ya kai ga shigar sojojin haya na kungiyar Wagner ta Rasha a yunkurin da ake yi na yakar ‘yan tawaye.

 

Putin ya bukaci a maido da tsarin mulki a Nijar, a daya bangaren kuma shugaban kungiyar Wagner Yevgeny Prigozhin ya nuna goyon bayansa ga juyin mulkin.

 

Wani abin sha’awa dai shi ne, an samu gagarumin rinjaye na goyon bayan Rasha a Nijar tun bayan juyin mulkin da aka yi a jamhuriyar Nijar, inda magoya bayan gwamnatin mulkin sojan kasar suka daga tutocin kasar ta Rasha.

 

 

Africanews/Ladan Nasidi.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *