Take a fresh look at your lifestyle.

Kotu Ta Wanke Tsohon Firayim Ministan Pakistan Khan daga tuhumar kisan kai – Lauya

Maimuna Kassim TukurAbuja Maimuna Kassim TukurAbuja

0 119

A ranar Litinin ne wata kotu a Pakistan ta yi watsi da zargin kisan kai da ake yi wa tsohon Firaminista Imran Khan, in ji lauyansa.

 

“Allah yabamu albarka,” in ji lauyan, Naeem Panjutha a dandalin aika sako na X, wanda akafi sani da Twitter, ya kara da cewa wata kotu ta kori tuhumar da ake yi da kisan wani lauya a Kudancin birnin Quetta.

 

Khan, wanda aka tuhume shi da kisan kai a watan Yuni, yana fuskantar shari’o’i sama da 100 tun bayan hambarar da shi a kuri’ar amincewa da majalisar dokokin kasar a watan Afrilu, 2022, bayan da ya yi karo da sojojin kasar.

 

Wata babbar kotu a Islamabad ita ma a yau litinin za ta yanke hukunci kan karar da Khan ya shigar na neman a dakatar da hukuncin da aka yanke masa kan wata shari’a da ake zarginsa da aikatawa.

 

 

 

REUTERS

Maimuna Kassim Tukur.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *