Rundunar Sojin Saman Najeriya NAF ta halakar da wasu kwamandojin Boko Haram biyu da ake nema ruwa a jallo tare da mambobinsu guda 40 a wani dakin ajiya da aka yi watsi da su a Kurebe, karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja.
Kakakin Rundunar Sojojin ta NAF, Air Commodore Wap Maigida, ya tabbatar da samun nasarar kai hare-haren ta sama, inda ya yi nuni da cewa, Rundunar Sojojin nasu za ta ci gaba da kai hare-hare kan mayakan na Boko Haram.
A cewar wani jami’in leken asiri na tsaro, ‘yan ta’addan; Abu Ubaida da Yusuf Abba sun gamu da ‘mummunan karshe’ a lokacin da jirgin NAF da ke aiki da rundunar ‘Operation Whirl Punch’ suka kai farmaki a unguwarsu kwanan nan.
“Za a iya tunawa cewa a ranar 22 ga watan Disamba, 2022, wani jirgin saman NAF ya kai hari kan taron ‘yan ta’adda a Kurebe a karamar hukumar Shiroro.
“An kashe ‘yan ta’adda da dama, amma ba’a san ko an kashe wani Kwamandan ‘yan ta’adda a harin da aka kai ta sama.
“Saboda haka, bayan wannan harin ta sama, binciken farko da aka yi ta hanyar amfani da majiyoyi da yawa ya nuna cewa akwai karkashin kasa a cikin ma’ajiyar inda ‘yan ta’addan ke gudu don buya a duk lokacin da jirgin NAF ya tashi a yankin.
“An kuma bayyana cewa ‘yan ta’addan sun yi shawagi a cikin wurin kuma ana ganin kekuna a lokuta daban-daban dauke da taki zuwa ma’ajiyar. “Wadannan takin da ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen kera abubuwan fashewar abubuwa (IEDs).
“Sakamakon haka, an aike da jiragen yaki na NAF domin tabbatar da lalata ma’ajiyar da kuma halaka ‘yan ta’adda,” in ji jami’in leken asirin.
Ya ce duk kwamandojin rundunar NAF bisa umarnin shugaban hafsan sojin sama, Air Marshal Oladayo Amao, suna tabbatar da cewa an hana ‘yan ta’adda da masu hada kai da duk wani abin shaka.
Leave a Reply