Take a fresh look at your lifestyle.

Kasar Japan Na Farautar Mutumin Da Ya Yi Barazanar Bam Ga Makarantu

Theresa Peter

0 239

‘Yan sandan Japan na ci gaba da farautar mutumin da ya aika da barazanar kisa ga daruruwan makarantu, lamarin da ya sa aka gaggauta rufe shi.

 

 

An aika da barazanar zuwa manyan makarantu da jami’o’i a farkon wannan makon daga lambar da aka yi wa rajista ta Tokyo.

 

 

Ba a samu fashewar abubuwa a gine-ginen makaranta ba, a cewar ‘yan sanda, kuma kawo yanzu babu wani rahoton harin da aka kai kan dalibai da ma’aikata.

 

 

‘Barazana bama-bamai’ ba kasafai ba ne a kasar Japan, wadda aka santa da karancin laifuka.

 

 

“Sakon farko ya fara ne a ranar Litinin, wanda ya isa makarantu da jami’o’i a fadin kasar.” A wata lardi, Saitama, sama da makarantu 170 ne suka fuskanci barazanar bam, in ji jami’ai.

 

 

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wani sako ya yi ikirarin cewa an tayar da bama-bamai sama da 330, yayin da wani ya ce: “Na dasa babban bam.”

 

 

Wasu rahotanni sun ce “sakwannin sun bukaci kudin fansa daga yen 300,000 (£1,870; $2,320) zuwa yen miliyan 3.”

 

 

A ranar Talata, an aike da sakonnin barazanar kashe dalibai da malamai da makamai na gida daga lamba daya zuwa manyan makarantu a larduna daban-daban da suka hada da Osaka, da Saitama da Ibaraki da ke kusa da Tokyo.

 

 

Barazanar ta ga an rufe makarantu da yawa a Japan a matsayin riga-kafi, kodayake yawancin an sake buɗe su a ranar Alhamis.

 

 

Har yanzu ana amfani da injin fax a Japan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *