Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kai wata ziyarar aiki a jihar Katsina

Kamilu Lawal,Katsina.

0 174

Ziyarar ta kwana biyu wadda shugaban ya kai na da nufin  kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da gwamnatin jihar ta gudanar kalkashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari

 

 

 

Shugaba Buharin dai ya sauka a filin jirgin sauka da tashin jirage na tunawa da Marigayi shugaban kasa Umaru Yar’adua a daren jiya laraba inda ya samu tarba daga gwamnan jihar Aminu Bello Masari da mataimakinsa Mannir Yakubu da wasu daga cikin mukarabban gwamnatin jihar

 

 

 

A rana ta farko, ana sa ran shugaban kasar zai bude wasu ayyuka da gwamnatin jihar ta gudanar domin inganta rayuwar al’ummar jihar

 

 

 

Daga cikin ayyukan da za zai kaddamar akwai aikin manyan gadojin kurde na kofar Kwaya da kofar Kaura a kwaryar birnin Katsina da aikin gyara da fadada babban asibitin Katsina

 

 

 

Akwai kuma aikin gadar sama na unguwar G.R.A. da cibiyar nazarin hasashen yanayi ta kasa watau Metrological Institute da sabon ofishin hukumar tara kudaden shiga na jihar

 

 

 

Kazalika, ana sa ran shugaban zai bude aikin samar da ruwan sha na kofar Kaura cikin birnin Katsina da  kanfanin sarrafa shinkafa na Darma Rice Mill, wanda hamshakin dan kasuwar nan Dahiru Mangal ya gina.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *