Kano: Kotu Ta Dawo Da Wali A Matsayin Dan Takarar Gwamna A PDP, Ta Kori Abacha
Aliyu Bello Mohammed, Katsina
A ranar Juma’a ne kotun daukaka kara ta Kano ta mayar da Sadiq Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano.
A ranar 22 ga watan Disamba, wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta bayyana Mohammad Abacha a matsayin zababben dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP tare da soke zaben fidda gwani da ya samar da Mista Wali a matsayin dan takara.
Sai dai a hukuncin daya yanke da mai shari’a Usman Musale, kotun daukaka kara ta ce jam’iyyar siyasa reshen jihar ba ta da hurumin gudanar da zaben fidda gwani.
Kotun ta ci gaba da cewa Mista Abacha ba zai iya tuhumar Mista Wali ba saboda bai shiga zaben fidda gwanin da ya gabatar da na karshe ba.
Leave a Reply