Take a fresh look at your lifestyle.

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Tsohon Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi

0 134

Shugaba Bola Tinubu ya gana da tsohon Sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi a fadar Shugaban Kasa a ranar 15 ga watan Yuuni.

Sarkin Kano na 14 ya isa fadar shugaban kasa da yammacin Alhamis da karfe 15:45 a agogon GMT.

Bayan isowarsa jami’an yarjejeniya ne suka tarbe shi, inda nan take suka shiga ofishin shugaban Najeriya.

Daga nan sai shugaban da bakon nasa suka shiga ganawar sirri bayan sun yi musayar yawu.

An zabi Lamido a matsayin Sarkin Kano na 14 a shekarar 2014 amma a shekarar 2020 gwamnatin jihar Kano ta tsige shi a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *