Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya isa kasar Guinea-Bissau domin halartar bikin cikar kasar shekaru 50 da samun ‘yancin kai da kuma ranar sojoji.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, shugaban na Najeriya zai hadu a ranar Alhamis, 16 ga watan Nuwamba, 2023, tare da sauran shuwagabannin gwamnatoci a Bisssu domin bikin, wanda shugaba Umaro Sissoco Embalo zai shirya.
President @officialABAT honours invitation to Guinea-bissau for Independence Day commemoration
President Bola Tinubu will, on Thursday, join other Heads of State and Government in Bissau, Guinea-Bissau, to celebrate the country’s 50th Independence Anniversary and Armed Forces… pic.twitter.com/0ZXBsVaSpU
— Presidency Nigeria (@NGRPresident) November 15, 2023
Guinea-Bissau ta yi bikin cika shekaru 50 da samun ‘yancin kai a ranar 24 ga Satumba, 2023, amma gwamnati ta sake tsara dukkan bukukuwan ranar 16 ga Nuwamba, 2023.
Ana sa ran shugaba Tinubu zai dawo Najeriya ranar Alhamis.
Ladan Nasidi.
Leave a Reply