Take a fresh look at your lifestyle.

Kotun Faransa Ta Daure Tsohon Kwamandan Laberiya

Usman Lawal Saulawa

0 244

Wata kotu a birnin Paris ta yanke wa wani tsohon kwamandan ‘yan tawayen kasar Laberiya hukuncin daurin rai da rai bisa samunsa da laifin aikata laifukan cin zarafin bil’adama a lokacin yakin basasar Laberiya.

 

Kunti Kamara babban jami’i ne a cikin ‘yan ta’addar Ulimo masu dauke da makamai, wadanda suka kula da mulkin ta’addanci a arewa maso yammacin Laberiya a shekarun 1990.

 

Shaidun gani da ido sun ba da shaida mai ban tsoro yayin shari’ar da aka shafe makonni uku ana yi.

 

Zarge-zargen da ake masa sun hada da kashe wani malamin makaranta a bainar jama’a, wanda zuciyarsa ya ci, da kuma bai wa sojojin da ke karkashinsa damar yi wa wasu ‘yan mata biyu fyade akai-akai.

 

Lauyoyin Mista Kamara sun yi zargin cewa shaidun da ake tuhumar sa ba su da inganci.

 

Rahoton ya ce an yi masa shari’a ne a Faransa saboda an kama shi a can, kuma dokar Faransa ta ba da damar a tuhumi manyan laifuffuka, ko da an aikata su a kasashen waje.

 

Kimanin mutane miliyan hudu ne aka kashe a rikicin kasar Laberiya cikin shekaru 10 daga 1993.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *