Take a fresh look at your lifestyle.

Mutane 19 ne suka mutu a Masar bayan da motar bas ta fado cikin mazarari

0 198

Ma’aikatar lafiya ta kasar Masar ta sanar da cewa, mutane 19 ne suka mutu, wasu 6 kuma suka samu raunuka, a lokacin da wata motar bas ta fada cikin mazarari a arewacin Masar a ranar Asabar.

 

Motar dai na dauke da mutane kusan 35 ne a lokacin da “ta bi ta kan wata babbar hanya ta fada cikin mazarari  ta Mansuriya da ke garin Aga,” a cikin lardin Daqahlia da ke arewacin kasar, a cewar majiyoyin tsaro.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *